DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Alhazan Nijeriya 1,622 sun isa birnin Madina a wannan Assabar – Hukumar NAHCON

-

Hukumar Alhazai ta Nijeriya NAHCON ta ce an kwashe mahajjatan Nijeriya 1,622 zuwa Madina domin gudanar da aikin Hajjin shekarar 2025.

Kamfanin dillancin labarai na Nijeriya NAN ya rawaito cewa mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima kaddamar da fara jigilar jirgi na farko a garin Owerri na jihar Imo a ranar Juma’a.

Bayanan da babban jami’in watsa labarai na hukumar NAHCON, Shafii Mohammed ya fitar, ya bayyana cewa, Jiragen Alhazan Nijeriya guda uku da sun yi jigilar jirage hudu a jihohin Bauchi, Kebbi, Imo, da Legas.

Mohammed ya ce jiragen sun hada da MaxAir, Flynas, da Kuma Air Peace. A ranar Juma’a jirgin MaxAir mai lamba VM3001 ya tashi daga Bauchi zuwa Madina da karfe 11:53 tare da alhazan Bauchi 539 da jami’ai shida.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara