DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

-

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan majalisar wakilai Muhammad Gudaji Kazaure.

A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na X jigo a jam’iyyar PDP ya bayyana tsare Kazaure a matsayin rashin bin doka da oda ne, ta hanyar kamawa da tsare ‘yan kasa ba tare da bin ka’ida ba.

Ya ba da misali da batun VeryDarkMan, wanda ya ce an sake shi ne bayan da jama’a suka nuna rashin jin dadinsu akan kama shi.

Atiku ya ce tun bayan kama tsohon dan majalisar a Kano aka garzaya da shi Abuja, har yanzu ba a gabatar da wata tuhuma ko yi wa iyalansa da lauyoyinsa da kuma al’ummar Najeriya karin bayani.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara