DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kano ta saki fursunoni mata 8 daga gidan gyara hali ciki har da masu juna biyu

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yi wa fursunonin afuwa ne a lokacin da ya kai ziyarar ba zata a gidan gyaran hali, tare da rakiyar wasu manyan jami’an gwamnati.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa makasudin ziyarar shi ne duba halin da fursunonin ke ciki da kuma lalubo hanyoyin da gwamnatin jihar za ta tallafa wa jin dadinsu.

Gwamnan ya nuna damuwarsa kan yawan fursunonin da ke jiran shari’a, inda ya ce daga cikin fursunoni 1,939, mutum 382 ne kawai aka yanke musu hukunci, yayin da 1,536 ke jiran shari’a.

Ya kuma ba da tabbacin cewa jihar za ta hada kai da bangaren shari’a domin a gaggauta yi musu da kuma rage cunkoso a gidan gyaran halin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Atiku Abubakar ya caccaki hukumar EFCC kan tsare tsohon dan majalisa Gudaji Kazaure

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya soki hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa ta EFCC, kan tsare tsohon dan...

Gwamnatocin Pakistan da Indiya sun amince da tsagaita wuta a Asabar dinnan

Ministan harkokin wajen Pakistan Ishaq Dar ya sanar a shafinsa na X cewa, kasashen sun amince da Shirin tsagaita wuta cikin gaggawa. Shugaba Trump ya sanar...

Mafi Shahara