DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Kano ta saki fursunoni mata 8 daga gidan gyara hali ciki har da masu juna biyu

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya yi wa fursunonin afuwa ne a lokacin da ya kai ziyarar ba zata a gidan gyaran hali, tare da rakiyar wasu manyan jami’an gwamnati.

A wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamna Yusuf ya bayyana cewa makasudin ziyarar shi ne duba halin da fursunonin ke ciki da kuma lalubo hanyoyin da gwamnatin jihar za ta tallafa wa jin dadinsu.

Gwamnan ya nuna damuwarsa kan yawan fursunonin da ke jiran shari’a, inda ya ce daga cikin fursunoni 1,939, mutum 382 ne kawai aka yanke musu hukunci, yayin da 1,536 ke jiran shari’a.

Ya kuma ba da tabbacin cewa jihar za ta hada kai da bangaren shari’a domin a gaggauta yi musu da kuma rage cunkoso a gidan gyaran halin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara