DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yawan tarin jam’iyyu na lalata gwamnati, in ji Ganduje

-

Shugaban jam’iyyar APC ta kasa Abdullahi Umar Ganduje, ya ce babu laifi a yi tsarin jam’iyya daya idan har hakan ne ‘yan Nijeriya ke so.

Ganduje ya bayyana hakan ne bayan jagorantar Sanatoci uku na jam’iyyar PDP daga jihar Kebbi zuwa wata ganawa da shugaban kasa Bola Tinubu a ranar Juma’a gabanin sauya shekar su zuwa jam’iyyar APC.

A cewar Ganduje, jam’iyyun siyasa da yawa suna lalata gwamnati.

Ya ce mafi yawan ‘yan jam’iyyun da suke dawowa jam’iyyar APC na komawa jam’iyyar saboda sunga kyakkyawan tsarin shugabanci da ke gudana a APC.

A cewarsa, kasar Sin tana daya daga cikin kasashe masu karfin fada aji a duniya, kuma tsarin jam’iyya daya ce suke amfani da shi dan haka ba abin kunya bane dan an yi tsarin jam’iyya daya a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwankwaso ba dan NNPP bane tun 2023, in ji shugaban jam’iyyar na kasa

Shugaban jam’iyyar NNPP na kasa, Dr. Agbo Gilbert Major, ya bayyana cewa Rabi’u Musa Kwankwaso, jagoran tafiyar Kwankwasiyya, ba halastaccen da jam’iyyar ne ba. Yayin da...

Sai kun kara damara wajen yaki da matsalar tsaro – Shugaba Tinubu ya umurci sojojin Nijeriya

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu, ya bukaci jami'an rundunonin tsaron Nijeriya da su kara azama wajen shawo kan kalubalen tsaro da kasar ke fuskanta. Shugaba Tinubu ya...

Mafi Shahara