DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Lauyoyi sun maka sanatoci a kotu don neman a karbo wani kaso na albashinsu saboda gazawa a aiki

-

Wata kungiya mai suna Association of Legislative Drafting and Advocacy Practitioners (ALDRAP) ta shigar da kara a gaban Kotun Kare Hakkin Masu Sayayya, tana neman tilasta wa sanatocin Najeriya mayar da wani kaso mai yawa na albashinsu tun daga 2023, bisa zargin rashin tabuka abin kirki a majalisa.

Kungiyar a cewaar rahoton da jaridar Punch ta fitar tana neman a karbo cikakken albashin sanatoci 40 da suka rike kujeru a Majalisar Dattawa da kuma Majalisun ECOWAS da Afirka, wanda suka yi rufa-rufa a aiyukan mazabunsu.

Google search engine

A cewar sanarwar da sakataren gudanarwa na ALDRAP, Amuga Williams, ya aika wa shugaban majalisar, Godswill Akpabio a ranar 26 ga Mayu, hakkin ‘yan Nijeriya ne su ci gajiyar ayyukan mazabu daga majalissa, kuma sun dauki matakin ne a madadinsu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara