DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar zabe ta kasa INEC ta sanya ranar gudanar da zabukan gwamna a jihohin Ekiti da Osun 

-

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmood Yakubu, ne ya bayyana hakan a ranar Juma’a, yayin rantsar da sabbin kwamishinonin zabe guda shida da majalisar dokoki ta kasa ta amince da su kwanan nan.

A cewarsa, za a gudanar da zaben gwamna a jihar Ekiti a ranar Asabar, 20 ga Yuni, 2026. Za a fara zaben fidda gwanin ‘yan takara na jam’iyyun siyasa daga ranar 20 ga Oktoba, 2025, sannan a kammala ranar 10 ga Nuwamba, 2025.

Google search engine

Hakanan, jam’iyyu za su rufe shigar da fom din ‘yan takara da yammacin ranar 22 ga Disamba, 2025.

A jihar Osun kuwa, za a gudanar da zaben gwamna a ranar Asabar, 8 ga Agusta, 2026.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara