DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna neman a yi wa marigayi DPO na Rano jihar Kano adalci – Wata kungiya

-

Kungiyar al’adu da ci-gaban kabilar Eggon, ta koka game da mummuna harin da ya kai ga rasa ran daya daga cikinsu wato, ASP Baba Mohammed, DPO din Rano.

Mohammed, dan asalin jihar Nasarawa, shi ne wanda wasu matasa suka far masa wanda hakan ya yi sanadiyar rasa ransa a Jihar Kano.

Google search engine

A cikin wani jawabi da kungiyar ta yi ma ‘yan jarida a garin Lafiya, Shugaban Kungiyar na kasa, Mandy Abuluya ya yi kira ga rundunar ‘yan sandan Nijeriya da ta yi bincike don gano wadanda suka aikata wannan barnar tare da hukunta su.

Mandy ya jajanta ma iyalan mamacin, da kuma kabilar Eggon, gwamnatin jihar da Shugaban ‘yan sandan Nijeriya game da lamarin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan sanda sun hana taron murnar zagayowar ranar haihuwar Peter Obi a Kaduna

Rundunar ‘yan sandan Jihar Kaduna ta hana wani taron da magoya bayan dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Labour a 2023, Peter Obi, suka shirya...

Jami’ar Kogi ta tabbatar da mutuwar malami a otel yayin da yake tare da wata ɗaliba

Rundunar 'yan sandan Jihar Kogi ta tabbatar da mutuwar Olabode Abimbola Ibikunle, malami a sashen kula da harkokin Jama'a na Jami’ar Prince Abubakar Audu, Anyigba. Rahotanni...

Mafi Shahara