DCL Hausa Radio
Kaitsaye

APC na cigaba da zawarcin Gwamnan Plateau na PDP

-

Kungiyar magoya bayan jam’iyyar APC ta yankin Arewa ta tsakiyar Nijeriya ta sake jaddada kiran da take yi ga Gwamnan Jihar Plateau Caleb Mutfwang, da ya fice daga jam’iyyar PDP ya koma APC, bisa umarnin shugabancin jam’iyyar na kasa.

Shugaban kungiyar, Alhaji Saleh Zazzaga, ne ya bayyana haka cikin wata sanarwa da ya fitar a Abuja, inda ya ce kiran na da nufin karfafa jam’iyyar APC gabanin zaben 2027.

Google search engine

Saleh Zazzaga ya ce wannan kira da suke yi yana bisa umarnin da suka samu daga sama.

Sanarwar ta ce Gwamna Caleb Mutfwang mutum ne mai kishin cigaba, kuma suna da yakinin cewa ya dace ya kasance cikin babbar jam’iyyar APC.

Ya kuma gargadi shugabannin jam’iyyar APC a Jihar Plateau da su guji nuna adawa da wannan yunkuri, yana mai cewa irin wannan adawa ba za ta haifar da da mai ido ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara