DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Borno ta bayar da tallafin Naira miliyan 300 ga mutanen da ambaliyar Mokwa ta shafa a jihar Neja

-

Gwamnan jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ne ya sanar da bayar da tallafin a lokacin da ya jagoranci tawagar jihar a ziyarar jaje a gidan gwamnati dake Minna.

Ya ce an bayar da tallafin ne domin kara wa kokarin gwamnatin jihar Neja wajen magance kalubalen da aka fuskanta.

Google search engine

Da yake jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar Neja, Farfesa Zulum ya bayyana cewa lokaci ya yi da ya kamata gwamnatocin kasashen duniya su hada karfi da karfe domin dakile illolin sauyin yanayi a cikin al’umma.

Ya kuma bukaci Gwamnatin Tarayya da ta samar da ingantaccen tsari wanda zai duba tare da magance matsalar sauyin yanayi a fadin kasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara