DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Bauchi za ta ƙirƙiri sabbin masarautu a jihar

-

Gwamnatin jihar Bauchi karkashin Gwamna Bala Abdulkadir Mohammed ta gayyaci al’umma a fadin jihar da su mika takardar neman kafa sabbin masarautu da gundumomi a jihar.

Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa dauke da sa hannun mai bai wa gwamna shawara na musamman kan harkokin yada labarai, Kwamared Mukhtar Gidado, ranar Litinin.

Google search engine

A halin yanzu dai jihar Bauchi tana da masarautu shida da suka hada da Bauchi, Katagum, Misau, Jama’are, Ningi da Dass.

Ko a watan Disamba 2024 gwamna Bala Abdulkadir ya amince da kafa masarautar Seyawa mai hedikwata a karamar hukumar Tafawa Balewa.

Solacebase ta rawaito cewa Muhammed ya bayyana hakan na daya daga cikin kokarin gwamnatin sa na ganin an samar da mafita ga matsalolin da suka dabaibaye na yunkurin samar da masarautar Seyawa, wanda ya gurgunta kokarin gwamnatocin da suka shude sama da shekaru talatin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar Dattijai ta mikawa shugaba Tinubu kudirin sake fasalin haraji domin amincewa

Majalisar dattijai ta mika kudirin dokar sake fasalin haraji zuwa ga shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu domin amincewa da aiwatarwa. Shugaban kwamitin majalisar kan yada labarai,...

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa...

Mafi Shahara