DCL Hausa Radio
Kaitsaye

INEC ta yi watsi da sanarwar taron NEC na Jam’iyyar PDP

-

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi watsi da sanarwar taron kwamitin zartarwa na kasa (NEC) karo na 100 da jam’iyyar PDP ta shirya gudanarwa a ranar 30 ga Yuni, tana mai cewa sanarwar ta saba ka’idoji.

A wata wasika da INEC ta aike wa jam’iyyar, mai dauke da sa hannun mataimakiyar sakatariyar hukumar, Hajiya Hau’ru Aminu, an bayyana cewa sanarwar bata cika sharuddan da ke sashe na 2(12)(3) na dokokin jam’iyyun siyasa na 2022 ba, wanda ke bukatar shugaban jam’iyya na kasa da sakataren jam’iyya su sanya hannu tare.

Google search engine

INEC ta shawarci PDP da ta bi ka’ida wajen gabatar da irin wannan sanarwa a nan gaba. Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da rikice-rikice ke ci gaba da ruruwa a cikin jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara