DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Cristiano Ronaldo ya tsawaita kwantiraginsa da kungiyarsa ta Al Nassr har zuwa shekarar 2027

-

Cristiano Ronaldo ya tsawaita kwantiraginsa da kungiyar Al Nassr ta kasar Saudiyya a hukumance, inda zai ci gaba da zama a birnin Riyardh na kasar har zuwa shekarar 2027.

Kungiyar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar a ranar Alhamis, inda a hoton Ronaldo yake rike da riga mai lamba “2027” tare da shugaban kungiyar Al Nassr, Abdullah Almajid.

Google search engine

Sanarwar ta tabbatar da cewa Ronaldo, wanda kuma ke rike da mukamin kyaftin din kungiyar, zai ci gaba da aiki tare da Al Nassr na tsawon shekaru biyu.

Ronaldo ya kuma bayyana jin dadinsa a wata sanarwa da ya wallafa a shafinsa na X.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara