DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya nada Ahmed Musa a matsayin manajan kungiyar Kano Pillars

-

Gwamnan Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya amince da sake fasalin hukumar gudanarwa ta ƙungiyar ƙwallon kafa ta Kano Pillars, tare da naɗa tsohon kyaftin ɗin Super Eagles, Ahmed Musa, a matsayin sabon Babban Manajan ƙungiyar.

Wannan sauyi na daga cikin matakan da gwamnatin jihar ke ɗauka domin farfaɗo da martabar ƙungiyar Kano Pillars, yayin da take shirin shiga sabuwar kakar gasar Nigeria Premier Football League (NPFL) ta shekarar 2025/2026.

Google search engine

Sanarwar da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar a ranar Juma’a, ta bayyana cewa an yanke wannan hukuncin ne bayan tattaunawa da masu ruwa da tsaki a harkar ƙwallon kafa, biyo bayan ƙarewar wa’adin hukumar da ta gabata wanda ya ɗauki shekara guda.

Sabuwar hukumar gudanarwar da aka ƙaddamar na da mambobi 17, inda Ali Muhammad Umar (Nayara) zai jagoranci hukumar a matsayin Shugaba, tare da sauran mambobi, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu is a highly skilled and experienced broadcast journalist and fact-checker. Ukashatu has over five years of experience in writing, editing, and presenting news and program content for radio and television. As a dedicated and hardworking professional, He is committed to upholding the values of accuracy, fairness, balance, independence, and accountability in her reporting and programs.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara