DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ku bari Shugaba Tinubu ya sauka a 2031 sannan ku jaraba sa’a – Sunday Dare ga masu hadakar ADC

-

Fadar Shugaban Ƙasa ta shawarci mambobin sabuwar gamayyar jam’iyyu da aka kafa ƙarƙashin tutar jam’iyyar ADC da su manta da zaɓen 2027, su mayar da hankali kan zaɓen 2031.

A ‘yan kwanakin da suka gabata ne wasu ’yan adawa ciki har da tsohon Mataimakin Shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar; tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, David Mark; tsohon Gwamnan Jihar Anambra, Mr Peter Obi; da kuma tsohon Gwamnan Jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, da wasu, suka haɗu a birnin Abuja inda suka bayyana jam’iyyar ADC a matsayin dandalin gamayya domin ƙwace mulki daga hannun Shugaba Bola Ahmed Tinubu.

Google search engine

Sai dai mai magana da yawun Shugaban Ƙasa, Sunday Dare, ya shawarci waɗanda ke jagorantar gamayyar da su jira, su gwada sa’ar su ne bayan Shugaba Tinubu ya kammala wa’adin mulkinsa na biyu.

Sunday Dare ya yi wannan magana ne a Abuja yayin da yake mayar da martani kan damuwar da ake nunawa game da yiwuwar gamayyar ta ƙwace mulki daga gwamnatin da jam’iyyar APC ke jagoranta.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara