DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisa ta gindaya sharuddan da Sanata Natasha za ta cika kafin a mayar da ita kan aiki bayan hukuncin kotu

-

Majalisar Dattawan Nijeriya ta gindaya wasu sharudda kafin ta dawo da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan kan kujerarta, bayan wata kotun tarayya da ke Abuja ta soke dakatarwar watanni shida da majalisar ta yi mata.

A hukuncin da ta yanke a ranar Juma’a, Mai shari’a Binta Nyako ta umurci Majalisar Dattawan da ta dawo da Sanata mai wakiltar Kogi ta Tsakiya, inda ta bayyana dakatarwar a matsayin mai tsanani da ya wuce kima.

Google search engine

Da yake mayar da martani kan hukuncin, mai magana da yawun Majalisar Dattawa, Sanata Yemi Adaramodu, ya ce ba za a dawo da Sanata Natasha kai tsaye ba.

Adaramodu ya bayyana cewa hukuncin kotu bai soke ikon tsarin kundin tsarin mulkin da ke ba Majalisar Dattawa damar ladabtar da mambobinta ba.

Ya kara da cewa Majalisar za ta sake zama domin tattauna batun ne kawai bayan Akpoti-Uduaghan ta cika umarnin kotu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara