DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu a tsaye yake kodayaushe don yakar matsalar tsaron da ya gada – Malam Nuhu Ribadu

-

Mai ba shugaban Nijeriya shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu, ya ce gwamnatin Shugaba Bola Tinubu ta dage wajen shawo kan matsalolin tsaro masu tsanani da ta gada.

Nuhu Ribadu ya bayyana hakan ne a wajen bikin cika shekaru 50 da kammala karatu na dalibai karo na 18 a kwalejin horar da hafsan sojoji ta Nijeriya (Nigerian Defence Academy, NDA) da aka gudanar a Abuja.

Google search engine

Ya ce a shekarar 2022, Nijeriya ta kasance a mummunan mataki na hadari, tana fama da dumbin kalubale da suka yi barazana ga hadin kan kasa, zaman lafiya da makoma.

Ya bayyana cewa kalubalen sun hada da matsalar ta’addanci a yankin Arewa maso Gabas, kashe-kashe da hare-hare a Arewa maso Yamma, rikice-rikice a yankin Neja Delta da kuma tashe-tashen hankula na ‘yan awaren kafa kasa a Kudu maso Gabas.

A cewarsa, gwamnatin Tinubu ta dauki matakai masu karfi wajen dawo da tsaro da kuma gina sabon kwarin gwiwar kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara