DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Za mu yi zanga-zanga tsirara idan ba a biya mana bukatunmu ba – Matan jihar Cross Rivers

-

Mata da matasan al’ummar Bendeghe Ekiem da ke ƙaramar hukumar Etung a Jihar Cross River sun ba Kwamishinan Noma, Johnson Ebokpo, wa’adin kwanaki 14 da ya janye shirin sayar da gonar gwamnati da ake shirin yin ruf da ciki, ko kuma su kasance cikin shiri don ganin mata sun yi tsirara su fita su yi rawa a cikin gonar koko.

An yanke wannan shawara ne a ranar Asabar yayin wata zanga-zanga da matasa da mata na al’ummar suka shirya domin nuna rashin jin daɗinsu game da batun.

Google search engine

A wata hira da jaridar PUNCH shugabar mata ta al’ummar, Ntunkai Obi, da kuma jagorar mata Helen Ogar, sun roƙi kwamishinan da ya tuntubi shugabannin al’ummar don su tattauna a kan batun, domin a tantance matakin da ya kamata a ɗauka na gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsohon sakataren gwamnatin Nijeriya Babachir Lawal ya fice daga APC

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Babachir David Lawal, ya bayyana ficewarsa daga jam’iyyar APC a hukumance, ta cikin wata wasika da ya aikawa shugaban jam’iyyar na...

APC ta sanar da fara sayar da fom din takarar zaben cike gurbi na majalisar tarayya

Jam’iyyar APC ta sanar da fara sayar da fom na neman takara da sha’awar zama ‘yan takara domin zaben cike gurbi na Majalisar Tarayya da...

Mafi Shahara