Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan ƙwallon ƙafa ta Nijeriya Super Eagles na bin bashi na alawus-alawus da wasu kudaden aiki.
Obi ya bayyana hakan ne cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na sada zumunta a ranar Talata, inda ya ce lamarin na iya rage wa ‘yan wasa ƙwazo da ƙwarin gwiwar wakiltar ƙasarsu da cikin himma.
Ya ce gwamnati na da alhakin kula da walwalar ‘yan wasa, tare da tabbatar da biyan hakkokinsu cikin lokaci da ƙarfafa musu gwiwa domin ci gaba da ba da gudunmawa ga ci gaban wasanni.



