DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sheikh Gumi ya musanta cewa ya gudu daga Nijeriya zuwa Turkiyya saboda barazanar Trump

-

Fitaccen malamin addinin Musulunci Sheikh Ahmad Gumi ya bayyana cewa tafiyarsa zuwa ƙasar Turkiyya ba ta da alaka da barazanar da Shugaban Amurka Donald Trump ya yi kan yiwuwar kai hari a Nijeriya saboda zargin kisan Kiristoci.

Jaridar The Guardian ta ruwaito cewa, bayan da hotunan Sheikh Gumi suka bayyana yana cikin ƙasar Turkiyya, wasu mutane a kafafen sada zumunta sun yada labarin cewa malamin ya gudu ne don tserewa hare-haren da ake zargin Amurka za ta kai Nijeriya.

Google search engine

Wasu masu amfani da dandalin X sun yi tsokaci suna cewa Gumi na iya zama cikin wadanda za su fuskanci hare-haren Trump, kasancewar an taba ganinsa yana tattaunawa da wasu ’yan bindiga a dazuka.

Sai dai Sheikh Gumi ya ce ya dade yana shirin tafiya tun kafin wannan barazana ta Trump.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Abin takaici ne a ce tawagar Super Eagles na bin bashi – Peter Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya na jam’iyyar Labour Party a zaɓen 2023 Peter Obi, ya bayyana takaici kan rahotannin da ke nuna cewa tawagar wasan...

Gwamnonin Kaduna da Sokoto sun bukaci a gaggauta samar da ‘yansandan jihohi

Gwamnan jihar Kaduna, Uba Sani, ya bukaci a kafa ‘yan sandan jihohi cikin gaggawa, yana mai cewa hakan ne kadai zai taimaka wajen kawo karshen...

Mafi Shahara