DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan Nijeriya sun gargadi Turai kan barazanar da Wike ke yi wa demokradiyya a ƙasar

-

Kungiyar Nigeria Unite ta kai karar minista Nyesom Wike zuwa ga Kungiyar Tarayyar Turai

Ministan Abuja Nyesom Wike ya dauko hanyar kassara dimukuradiyya a Nijeriya. Wannan shi ne babban zargin da ke cikin wata zungureriyar wasika da ƙungiyar ta “Nigeria Unite” ta gabatar ga   shugabar hukumar gudanarwa ta Tarayyar Turai, Ursula von der Leyen. Kungiyar mai rajin kare dimukuradiyya ta  nuna tsananin damuwa cewa dimokuradiyya a Nijeriya na dab da rugujewa — tare da zargin cewa Ministan Abuja, Barrister Nyesom Wike, na mamaye siyasa da karya tsarin mulkin Nijeriya.

A cikin wasikar da aka aika ranar 11 ga Nuwamba 2025, ƙungiyar ta ce halayen Wike da goyon bayan da yake samu daga gwamnatin tarayya sun jefa Nijeriya cikin hanyar zama ƙasar jam’iyya ɗaya, lamarin da ke shafar dimokuradiyya gaba ɗaya a kasashen yankin Sahel.

A cewar wasikar, Wike ana zarginsa da:

damfarar tsarin siyasa,

tsoratar da ‘yan adawa,

sayen hukumomi da alkalai,

murƙushe jam’iyyun PDP, LP da ADC,

kulle ofisoshin jam’iyyun adawa da amfani da albarkatun gwamnati don rushe su,

da kuma amfani da ’yan sanda, wasu alkalan tarayya, da ma’aikatan INEC wajen murde tsarin siyasa.


Wasikar ta ce dabi’un ministan na Abuja sun kai ga samar da :

rabuwar kawuna a tsakanin ‘yan majalisar Rivers saboda rikicinsa da Gwamna Sim Fubara,

ƙone majalisar dokoki da rikice-rikicen doka,

tilasta wa gwamnoni, sanatoci da manyan jam’iyyun adawa shiga APC,

da kuma karkatar da dimokuradiyya zuwa salon mulkin kama-karya.


Ƙungiyar ta gargadi cewa yadda “APC ke amfani da barazana, cin hanci, da cin zarafi don murƙushe adawa” na nuna cewa Nijeriya na dab da zama ƙasar jam’iyya ɗaya — abin da ka iya haifar da tarzoma da tashin hankali kafin zaɓen 2027.

Wasikar ta da kungiyar Nigeria ta aike wa kasashen Turai ta kuma zargi Majalisar Dokokin Nijeriya da zama mai “rauni kuma a ƙarƙashin ikon shugaba  Tinubu,” ta ce rashin sa hannun su wajen tsare doka da oda ya ƙara buɗe ƙofa ga zalunci da karya tsarin mulki.

A cikin buƙatunta, ƙungiyar Nigeria Unite ta roƙi Tarayyar Turai, Majalisar Dinkin Duniya, Amurka da Birtaniya su sa baki cikin lamarin, su sanya takunkumi kai tsaye kan Nyesom Wike, da kuma wasu alkalan da ake zargi suna taimaka masa.

Wasikar ta yi gargadin cewa duk wata rugujewar dimokuradiyya a Nijeriya — ƙasa mai mutane miliyan 250 — ka iya haifar da girgizar siyasa da tsaro a yammacin Afirka, ta ƙara yawan kwararar ’yan gudun hijira, ta kuma haifar da barazana ga Turai da Amurka.

A ƙarshe, ƙungiyar ta ce lokaci ya yi da kasashen duniya ya kamata su tashi tsaye domin “kare dimokuradiyya kafin lamarin ya rikide ya zama abin tsoro.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Libya ta kora ‘yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka’ida ba a kasar

Hukumomin Libiya sun kori ’yan Nijeriya 80 daga ƙasar bayan kama su suna zama ba bisa ƙa’ida ba, a wani yunkuri na rage cinkoso a...

Majalisar dattawan Nijeriya na shirin haramta daukar ‘yan kasa da shekaru 18 aikin soji

Majalisar dattawan Nijeriya na shirin amincewa da kudurin da zai haramta daukar mutane 'yan ƙasa da shekaru 18 a aikin soja. Sanata Abdulaziz Yar’Adua daga Katsina...

Mafi Shahara