DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sojoji sun dakile yunkurin garkuwa da ‘yan bautar kasa

-

Dakarun haɗin gwiwa na “Operation Hadin Kai” sun dakile wani yunkurin garkuwa da masu yi wa kasa hidima 74 a hanyar Buratai zuwa Kamuya, jihar Borno.

Mai magana da yawun rundunar, Manjo Sani Uba ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a yau Alhamis, inda ya ce sojojin sun yi gaggawar kai dauki bayan motocin ɗaliban sun lalace a wurin da ake yawan yin garkuwa da mutane.

Google search engine

A cewar sa, masu yi wa kasa hidimar maza 36 da mata 38, motar tasu ta lalace ne da misalin ƙarfe 9:05 na dare a ranar Talata.

Sojojin sun gano matasan suna cikin haɗari, suka garzaya suka kwashe su zuwa sansanin soja da ke Buratai don kare su daga yiwuwar hare-haren ‘yan ta’addan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ƴan Nijeriya sun gargadi Turai kan barazanar da Wike ke yi wa demokradiyya a ƙasar

Kungiyar Nigeria Unite ta kai karar minista Nyesom Wike zuwa ga Kungiyar Tarayyar Turai Ministan Abuja Nyesom Wike ya dauko hanyar kassara dimukuradiyya a Nijeriya....

Libya ta kora ‘yan Nijeriya 80 gida saboda zama ba bisa ka’ida ba a kasar

Hukumomin Libiya sun kori ’yan Nijeriya 80 daga ƙasar bayan kama su suna zama ba bisa ƙa’ida ba, a wani yunkuri na rage cinkoso a...

Mafi Shahara