DCL Hausa Radio
Kaitsaye

’Yan bindiga sun yi ajalin mutane 33 a jihar Kebbi

-

Rundunar ’yan sandan jihar Kebbi ta tabbatar da mutuwar mutane 33 sakamakon harin da wasu da ake zargin ’yan bindiga ne suka kai a Bui da ke karamar hukumar Arewa ta jihar.

Mai magana da yawun rundunar ’yan sandan jihar, SP Bashir Usman, ya bayyana cewa bincike ya nuna maharan na shigowa yankin ne daga karamar hukumae Gudu da ke jihar Sokoto State.

Google search engine

Ya ce bayan harin, mazauna ƙauyukan Mamunu, Awasaka, Tungan Tsoho, Makangara, Kanzo, Gorun Naidal da Dan Mai Ago sun tashi tsaye domin kare kansu, abin da ya jawo artabu mai tsanani da ya yi sanadin mutuwar mutane 33.

A cewar sa ’yan sandan tare da sojoji da sauran hukumomin tsaro sun ƙara tura jami’ai da kayan aiki zuwa yankin, tare da ci gaba da sintiri domin dawo da zaman lafiya da hana sake faruwar irin wannan hari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya yi kira da a zauna lafiya gabanin zaɓen Abuja, Kano da Rivers

Shugaban Ƙasa, Bola Ahmed Tinubu, ya yi kira ga masu kaɗa ƙuri’a, jami’an tsaro da jami’an Hukumar zaɓe Mai zaman kanta (INEC) da su gudanar...

Gwamnatin Nijeriya za ta kafa kwalejin koyon likitanci ta sojoji don magance karancin likitoci

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da shirin kafa kwalejin koyon likitanci ta soji "Armed Forces College of Medicine and Health Sciences" a matsayin wani mataki na...

Mafi Shahara