Gwamnatin jihar Borno ta tattaro kwararrun maharba sama da 2,000 domin su yaki kungiyar Boko Haram.
Ana sa ran daga yanzu maharban za su iya shiga daji don yaki da yan Boko Haram kamar yadda gidan rediyon DW ya tabbatar a ranar Juma’a.
A yan kwanakin nan dai Boko Haram ta na kokari kai hari an sojoji domin nunawa duniya cewa har yanzu suna da tasiri. Amma hukumomi sun ce kada kowa ya tada hankalin shi.
Ya kuke kallon wannan yunkurin?
