Mai mana sharhi Ishaq Idris Guibi ya rubuta a shafinsa na sada zumunta cewa:
Yawancin ma’aikatan gwamnatin tarayya na korafin yau daya ga watan Mayu, ba dilin-dilin babu dalilinsa duk da Baba Buhari ya ba da umarni tun 23 ga watan jiya a hanzarta biya. Su kuwa malaman jami’a sun shiga wata na hudu ke nan ba dilin-dilin.
