Kotun sauraren kararrakin zaben gwamnan jihar Bayelsa ta soke zaben gwamna Duoye Diri da mataimakinsa LawrenceEwhrudjakpo.
Alkalai 3 da suka yi shari’ar karkashin jagorancin mai shari’a Ibrahim Surajo, ta soke zaben bayan takardar koken da dan takarar jam’iyyar ANDP ya kai, na cire jam’iyyarsu daga zaben da ya gudana a 16, ga watan Nuwambar bara 2019.
Alkalan sun yanke cewa a gudanar da sabon zabe cikin watanni 3.
