DCL Hausa Radio
f DCL HAUSA FACEBOOK
Saturday, April 18, 2026
HomeUncategorizedLikitoci da sauran malaman asibiti ne ba su cika karbar cin hanci...

Likitoci da sauran malaman asibiti ne ba su cika karbar cin hanci da rashawa ba – Kungiyar NMA

Kungiyar likitocin Nijeriya ta NMA ta bayyana cewa sabon rahoton baya-bayan nan ya nuna yadda aka gano likitoci da sauran malaman asibiti da aka ce ba su cika karbar cin hanci da rashawa ba a wajen aikinsu sabanin ma’aikatan sauran wasu bangarori.

Shugaban kungiyar na kasa Prof Bala Audu ya bayyana wannan kididdigar a yayin wata zantawa a Abuja.

Binciken kamar yadda jaridar Daily Trust ta rawaito ya nuna cewa kusan kaso 30% na mutanen Nijeriya na zuwa neman magani wajen likitoci da sauran malaman asibiti kuma ba su biyan wani cin hanci kuma ba a ma neman su biya wani cin hanci.

Sai dai Prof Audu ya ce kaso 4% ne kacal aka ba da cin hanci ga likitoci da malaman asibiti kuma ya ce za su yi kokarin rage yawan wannan adadin.

RELATED ARTICLES

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Most Popular

Recent Comments

Mustapha madu bande on Tarihin marigayi Aminu Dantata