Muneerat Abdussalam da ke da shafuka a shafukan sada zumunta wacce ke koyar da ilimin Jima’i ƙarara ta bar addinin musulunci.
Muneerat ta yi shekaru biyu ne rak a cikin addinin na musulunci, kuma ta rubuta a shafinta na Facebook inda take cewa :
“Daga yau bana fatan alaƙanta kai na da addinin musulunci, saboda tsawon shekaru 2 da na yi a cikinsa ban sami komai ba hasali ma sai barazanar kisa, zagi da ake yiman, sanna musulmai ba su taɓa yarda da gaske ko nuna min wani irin soyayya ba, a matsayina na marainiya, shiyasa na ji bazan iya jure hakan ba, na gaji.
