Majalisar dokokin jihar Bauchi ta yi kira ga gwamnatin jihar da ta sanya wa babban asibiti na garin Azare da ke jihar sunan marigayi Ali Kwara.
Dan majalisa Tijjani Aliyu mai wakiltar mazabar Azare/Madangala ne ya gabatar da kudirin a zauren majalisar dokokin.
Tijjani Aliyu yace marigayi Alhaji Ali Kwara gwarzo ne wanda tarihi ba zai manta da shi ba, saboda ya sadaukar da rayuwarsa, dukiyarsa don tabbatar da jihar Bauchi da Nijeriya sun zauna lafiya.
