DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa ta haramtawa mata musulmai sanya Hijabi a cikin makarantu

-

Gwamnatin kasar Faransa ta haramtawa mata Musulmai amfani da Hijabi, abaya ko kuma rufe kan su a cikin makarantu.

Google search engine

Tuni dai wannan sabuwar doka ta fara cin karo da suka daga kungiyoyin kare hakkin addinai da dai-daikun mutane, duk da cewa gwamnatin kasar ta ce ta yi haka ne don kare mata Musulman.

Wannan na zuwa ne bayan da cin zarafi da kuma kyamar mata musulmai ke kara ta’azzara a kasar da  ta yi kaurin suna wajen kyamatar addinin musulunci

Ta cikin sanarwar da gwamnatin ta fitar, ta ce mata musulmai a kasar na fuskantar kyara, tsokana da kuma cin zarafi musamman a tsakanin abokan karatun su da malamai a cikin makaratu, a don haka hana su sanya Hijabi ko kuma rufe gashin su ne kadai hanyar da zai sa su saje da sauran dalibai da nufin gujewa cin zarafi.

Sanarwar ta kuma kara da cewa bai kamata a ce da zarar malami ya shiga aji ya gane daliba musulma da wadda ba musulma ba.

Tun ba yanzu ba, malamai a kasar sun sha yin korafin cewa gane banbanci tsakanin daliban su musulmai da wadanda ba musulmai ba, yana hana su gudanar da aikin su yadda ya dace saboda irin ba banbancin mu’amala da ke tsakanin mabanbantan addinan.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara