DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Uganda ta zartas da hukuncin kisa kan matashin da aka samu da auren jinsi

-

Google search engine

Mahukuntan kasar Uganda sun yankewa mutum na farko hukuncin kisa a tarihin kasar, bayan kama shi da laifin take dokokin da suka haramta auren jinsi.

Wannan shi ne karo na farko da kasar ta zartas da hukuncin da take ikirarin dauka duk da yadda kasashen yammacin duniya suka yi watsi da wannan mataki.

Dokar dai ta tanadi daurin rai da rai idan aka kama mutane biyu da laifin auren jinsi, sannan ta tanadi hukuncin kisa kai tsaye idan aka sake kama su a karo na biyu, ko kuma suka yiwa wani irin wannan dabi’a ta dole har ya kamu da cuta, ko kuma tilastawa karamin yaro ko tsoho ko masu bukata ta musamman.

Rahotanni sun ce tuni aka zartas da hukuncin kisan kan matashin mai shekaru 20, bayan an same shi da laifin maimaita luwadin bayan kamun da aka yi masa na farko da wani mutum mai shekaru 41.

Tuni dai shugaban kasar dama ‘yan majalisa suka fara shan suka, kan wannan mataki da suka dauka, wanda ake ganin yana da matukar tsauri.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Muna da hujja ba a makance muke goyon Tinubu ba – Kungiyar Disciples of Jagaban

Kungiyar magoya bayan shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ta Disciples of Jagaban ta ce ba a makance ta ke nuna goyon baya ga shugaban ba,...

Rundunar sojin Nijeriya ta sulhunta kabilun da ke rikici a Taraba

By Salisu Ado Sulaiman Rundunar sojin kasan Nijeriya ta jagoranci zaman sulhu tsakanin kabilun da ke rikici a jihar Taraba. Kwamandan rundunar Operation Whirl Punch Brigadier Janar...

Mafi Shahara