DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun koli ta kori karar da ke neman a sauke Shugaba Tinubu

-


Google search engine

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da aka shigar kan Shugaba Bola Tinubu akan zarge-zargen tu’ammali da miyagun kwayoyi da kuma binciken hukumar leken asiri ta Amurka CIA.

Karar wadda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar HDP a shekara ta 2019 Ambrose Aworu ya shigar, ya nemi kotu ta sauke Shugaba Tinubu.

Sai dai a hukuncin kotun mai alkalai biyar, karkashin jagorancin Mai Shari’a Uwani Abba-Aji, ta yi watsi da karar da tace ba ta da tushe kuma ta ci tarar Ambrose Aworu naira miliyan 5. Hakama ta umurci akawun kotun kar ya koma karbar irin wannan karar daga wanda ya shigar da ita Ambrose Aworu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Wasu tsoffin ‘yan majalisar dokokin Kano sun yi mubaya’a ga Barau Jibrin a takarar gwamna a 2027

Wasu tsoffin 'yan majalisar dokokin jihar Kano da kuma masu ci a yanzu sun mara wa mataimakin shugaban majalisar dattawan Nijeriya Barau Jibrin baya don...

Gwamnati ta binciki ta’azzarar matsalar tsaro a Nijeriya – Kwankwaso

Tsohon gwamnan jihar Kano Rabi'u Musa Kwankwaso ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya ta da gudanar da bincike kan musabbabin ta'azzarar matsalar tsaro a wasu...

Mafi Shahara