DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta Nijeriya na son a rage ƙarin kudin kira da na data zuwa kashi 10 ko su tafi kotu

-

Kungiyar masu amfani da layukan sadarwa ta Nijeriya NATCOMS ta ce za ta dauki matakin shari’a kan hukumar sadarwar Nijeriya NCC, biyo bayan kin amincewar bukatar rage karin kudin kira da data daga kaso 50 zuwa kaso 10.
Yayin zantawarsa da jaridar Punch a ranar Talata, shugaban kungiyar Adeolu Ogunbanjo ya ce halin ko in kula na NCC ya jefa masu amfani da layukan sadarwa cikin zulumi na karin kudaden.
“Mun basu zuwa jiya Talata cewa su fada mana matsayarsu amma har yanzu shiru, ba don haka zamu garzaya zuwa kotu a yau Laraba” in ji Adeolu.
Kungiyar ta NATCOMS na wakiltar al’ummar Nijeriya Miliyan 157 dake amfani da layukan sadarwa daban-daban.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

‘Yan bindiga sun hallaka manoma 32 a jihar Niger

Akalla manoma 32 ne aka hallaka a hare-haren da ’yan bindiga suka kai kan al’ummomin Tugan-Makeri, Konsoko da Pissa a karamar hukumar Borgu ta Jihar...

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Mafi Shahara