DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Akwai bukatar hukumar NAHCON ta mayar wa maniyyatan hajjin bana naira 400,000 – Kungiyar IHR

-

Kungiyar “Independent Hajj Reporters” mai sanya ido kan harkokin aikin hajji ta yi kira ga hukumar alhazzan Nijeriya da ta mayar wa maniyyata aikin hajjin bana naira N437,000 kowannensu, bayan da aka samu saukar farashin dala a kasuwar canji.
A cikin wata sanarwa da kungiyar ta fitar, ta ce binciken da ta yi akan bayanan kudin aikin hajjin 2025 da hukumar NAHCON ta fita, ta gano cewa ya kamata kowane maniyyaci a mayar masa da rarar kudin da ya biya.
Sai dai a martanin da suka mayar, bangaren yada labarai na hukumar NAHCON sun bayyana cewa, sabanin fahimtar kungiyar IHP duk wani sauyi da aka samu a canjin kudi bayan an kayyade kudin aikin hajji, kai tsaye ba ya nufin za a mayar wa mahajjata kudin.
Bangaren yada labaran sun kara da cewa hukumar NAHCON ta yi alkawalin bin ka’ida wajen mayar wa mahajjata kudin su idan aka samu wani ragi.

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kwamishinan Jigawa ya mayar da rarar Naira miliyan 301 daga kudaden da aka ware don shirin ciyar da al’umma a watan Ramadan

Kwamishinan ayyuka na musamman na jihar Jigawa, Alhaji Auwalu Danladi Sankara, ya mayar da Naira miliyan 301 zuwa baitul malin jihar, daga cikin Naira biliyan...

Gwamnatin mulkin sojin Nijar ta karɓi wasikun kulla kawance daga sabbin jakadun ƙasashe 8

A ranar Juma’a, 9 ga Mayu, 2025, fadar gwamatin ta Jamhuriyar Nijar ta karɓi sabbin jakadun daga jakadun ƙasashen duniya guda takwas. Inda shugaban mulkin sojin...

Mafi Shahara