Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda za su dauki takobi
Jihohin hudu sun hada da Agadez, Diffa, Tillaberi da babban birnin Niamey
Cikin jimillar ‘yan kokawa 80 da suka fito daga jihohi takwas na kasar ya zuwa wannan rana ta uku, 12 suka rage.
Jihar Maradi ce ke kan gaba da yawan ‘yan kokawar cikin wadanda ba su fadin ba inda take da biyar yayin da jihar Tahoua ke biya mata da mutum hudu, sai jihar Dosso da biyu sai kuma ta karshe Zinder da mutum daya.
Tuni zakaran gasar kokawar na bara Abba Ibrahim na babban birnin Yamai ya sha kasa tun a kwana na biyu na gasar ta 2025.



