Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya amince da biyan N50,000 duk wata ga matasan yankin Neja Delta su 10,000 domin rage wahalhalun da kasar ke ciki.
Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio, ne ya bayyana hakan a yayin taron wayar da kan kabilu da matasa da mata na yankin Neja Delta a Fatakwal a ranar Talata.
Ya ce za a biya kudin ne a karkashin shirin NDDC Youth Intensive Scheme kuma zai dauki tsawon watanni 12 na farko tare da yiwuwar tsawaitawa.


.jpeg)


Arewa kumafa