DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wasu jiga-jigan jam’iyyar APC a yanki Arewa sun fara tallata tazarcen shugaba Tinubu a 2027

-

An jiyo wasu manya-manyan jiga-jigan jam’iyyar APC sun fara yakin neman zaben shugaba Tinubu karo na biyu na zaɓen a 2027

Google search engine

Jiga-jigan sun hada da shugaban jam’iyyar na kasa, Abdullahi Ganduje da sakataren gwamnatin tarayya George Akume, sun yi kira ga shugaba Tinubu da ya sake tsayawa takara a karo na biyu.

A kwanakin baya dai shugaban jam’iyyar na kasa Abdullahi Ganduje ya bukaci ‘yan siyasar Arewa da suyi hakuri a zaben 2027 su bai wa shugaba Tinubu ya ida wa’adinsa na biyu.

Shima sakataren gwamnatin tarayya George Akume, yayin da yake magana a wani shirin gidan talabijin na TVC, ya shawarci ’yan Arewa da kada su nemi kujerar shugaban kasa a 2027 su bari sai shekarar 2031.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara