DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Hukumar Zaben Nijeriya na son ayi dokar da za ta hana zuwa da sama da naira dubu 50 a rumfar zabe

-

Hukumar zabe mai zaman kanta a Nijeriya INEC ta bukaci majalisa ta yi dokar haramta zuwa da kudade masu yawa a rumfunan zabe domin magance matsalar sayen kuri’a da kuma magudin zabe.
Daraktan sashen dokoki na hukumar Tanimu Muhammed, SAN, ne ya yi wannan kiran a yayin wani taron kan sake gyaran dokokin zabe da kwamitin majalisar wakilai kan zabe ya shirya a Abuja.
Tanimu Muhammed ya bukaci ‘yan majalisa da su fito da dokar da zata saka naira dubu hamsin a matsayin mafi karancin kudin da mutum zai iya rika wa a kusa da rumfunan zabe.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai yiwuwar madugun adawar Kamaru Isa Tchiroma yana Nijeriya ya boye – Rahotanni

Madugun adawar Kamaru, Issa Tchiroma Bakary, wanda ya kalubalanci nasarar Paul Biya, yana iya kasancewa yana a Nijeriya kamar yadda Africa Intelligence ta ce, amma...

Fusatattun matasa sun hallaka limamin masallaci a jihar Kwara bisa zargin maita

Wasu fusatattun matasa a garin Sokupkpan da ke ƙaramar hukumar Edu a jihar Kwara sun hallaka limamin masallacin yankin, Malam Abdullahi Audu, bisa zargin cewa...

Mafi Shahara