DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotun koli ta kori karar da ke neman a sauke Shugaba Tinubu

-


Google search engine

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da aka shigar kan Shugaba Bola Tinubu akan zarge-zargen tu’ammali da miyagun kwayoyi da kuma binciken hukumar leken asiri ta Amurka CIA.

Karar wadda dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar HDP a shekara ta 2019 Ambrose Aworu ya shigar, ya nemi kotu ta sauke Shugaba Tinubu.

Sai dai a hukuncin kotun mai alkalai biyar, karkashin jagorancin Mai Shari’a Uwani Abba-Aji, ta yi watsi da karar da tace ba ta da tushe kuma ta ci tarar Ambrose Aworu naira miliyan 5. Hakama ta umurci akawun kotun kar ya koma karbar irin wannan karar daga wanda ya shigar da ita Ambrose Aworu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jihohin APC sun sake mara wa Tinubu baya matsayin dan takara a zaɓen 2027

Jam’iyyar APC a jihohi da dama ta sake bayyana goyon bayanta ga shugaba Bola Tinubu, a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar a zaben...

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Mafi Shahara