DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda fitinar bayan zabe ta yi ajalin mutane sama da 700 a Tanzaniya

-

Jam’iyyar adawa ta Chadema a Tanzaniya ta bayyana cewa fiye da mutane 700 ne suka mutu cikin kwana uku na zanga-zangar bayan zaɓen shugaban ƙasa, wadda ta haifar da tarzoma da tsaurara matakan tsaro a fadin ƙasar.

A cewar rahoton jaridar Daily Trust, zaɓen ya gudana ne cikin tashin hankali, katsewar intanet da kulle hanyoyin sadarwa, lamarin da ya sa ake diga ayar tambaya kan sahihancin zaɓen da gaskiyar sakamakon.

Google search engine

DCL Hausa ta ruwaito cewa, shugabar Tanzaniya Samia Suluhu Hassan, mai shekara 65, wadda ke neman wa’adin farko cikakke a ƙarƙashin jam’iyyar Chama Cha Mapinduzi (CCM), ta fuskanci hamayya daga ‘yan takara 16. Sai dai hana wasu manyan ‘yan adawa shiga takara da shari’o’in da ke ci gaba, sun jefa shakku cikin tsarin.

Kakakin jam’iyyar Chadema, John Kitoka, ya shaida wa kamfanin dillancin labaran Faransa na AFP cewa adadin mutanen da suka mutu a babban birnin kasar, Dar es Salaam ya kai kusan 350, yayin da a a birnin Mwanza ya wuce 200. AFP ya ce jimillar ta kai kusan 700, kuma “na iya ƙaruwa” saboda an kafa dokar hana fita da dare tun ranar Laraba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara