DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dikko Radda ya nada sakataren gwamnatin Katsina da wasu mukamai 10

-

Google search engine

Sabon Gwamnan jihar Katsina Malam Dikko Umaru Radda ya amince da nadin Arch Ahmad Musa Dangiwa a matsayin sakataren gwamnatin jihar.

A cikin wata sanarwa da Dikko Radda ya sanya wa hannu, ta ce Gwamnan ya kuma nada Jabiru Tsauri a matsayin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati. Kazalika, sanarwar ta ce, Gwamnan ya nada Barr Mukhtar Aliyu a matsayin mataimakin shugaban ma’aikatan gidan gwamnati, sai Abdullahi Aliyu Turaji a matsayin PPS.

Sauran nade-naden su ne na Malam Maiwada Danmalam a matsayin Darakta Janar mai kula da kafafen yada labarai, Sai Ibrahim Kaula Mohammed a matsayin mai magana da yawun Gwamna da Abubakar Badaru Jikamshi a matsayin mataimaki na musamman ga Gwamna kan kafafen yada labarai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara