DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yajin aikin da za ku tsunduma haramtacce ne, sakon FG ga kungiyar NLC

-

Gwamnatin Nijeriya ta sanar da kungiyar kwadago ta kasa NLC cewa yajin aikin da take shirin fadawa ya kan halin matsin tattalin arziki da tsadar rayuwa haramtacce ne kamar yadda doka ta sanar.
Jaridar Punch ta rawaito cewa kungiyar kwadago ta NLC ta ba gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki 7 da ta soke aniyarta kan duk tsare-tsaren da suka jefa talakawa cikin mawuyacin hali ko kuma a fuskanci mummunan yajin aiki a kasar.
Sai dai, babbar Sakatariya a ma’aikatar shari’a ta kasar Mrs B.E Jeddy Agba ta sanar cewa kotun kula da ma’aikata ta kasa ta haramta tafiya wannan yajin aiki mai dangane da cire tallafin man fetur.
Ta ce a ranar 5 ga watan jiya na Yuni, kotu ta dakatar da kungiyar kwadago na tafiya yajin aiki.
Sanarwar ta shawarci kungiyar kwadagon da ta bullo da wasu sabbin dabaru ba wai na yajin aiki ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara