DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin jihar Kano ta gayyaci matashin da ya tsinci Naira Miliyan 15 kuma ya mayarwa mai shi

-

Google search engine

Majalisar dokokin jihar Kano ta
gayyaci matashi Auwalu Salisu da ke sana’ar tuka babur din adai-daita Sahu,
bayan da ya mayar da wasu makudan kudade har naira miliyan 15 ga wani fasinjan
sa dan asalin kasar Chadi.

Wannan na zuwa ne bayan bukatar hakan da dan
majalisa mai wakiltar karamar hukumar Doguwa Alhaji Salisu Muhammad ya gabatarwa
majalisar, yayin zamanta na yau, karkashin jagorancin shugabanta Alhaji Isma’il
Jibril Falgore.

Majiyar DCL Hausa ta Daily Trust ta ruwato cewa matashin  mai shekaru 22 ya mayar da kuddaden ne bayan
da fasinjansa ya manta da su a cikin adai-daita sahun sa.

Yayin zaman majalisar, dan majalisa Muhammad ya ce matashin
ya nuna tsantsar tawakkali da kuma hali na gari wajen mayar da kudaden idan aka
yi la’akari da halin matsin da ake ciki, a don haka ya kamata majalisar ta
karrama shi.

Wannan ce ta sa shugaban majalisar ya amince da bukatar, yayin
da ya amince a gayyaci matashin sannan yayi alkawarin cewa majalisar zata
tallafa masa.

Dukannin mambobin majalisar 44 sun amince da wannan
bukata, a cewar su wannan zai karfafawa sauran matasa gwiwa kan su rika sanya
gaskiya cikin harkokin su na yau da kullum.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara