DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sabuwar Zanga-zanga ta barke a Kano

-

 

Google search engine

Sabuwar zanga-zanga ta barke a
jihar Kano, yayin da jama’a ke ci gaba da nuna fushin su kan hukunci kotun
daukaka kara da ta ayyana Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben
bana, a maimakon Abba Kabir Yusuf da hukumar zabe ta INEC ta sanar.

 

Wannan ba ita ce zanga-zanga ta
farko da al’umma a jihar ke gudanarwa ba, cikin makonni biyu da suka wuce,
yayin da suke ganin shari’ar na cike da kura-kurai musamman bayan bullar
takardun kotu da ke nuna cewa Abba Kabir Yusuf ne ya yi nasara ba Nasiru Gawuna
ba.

 

Duk da kotun daukaka karar ta
fitar da sanrwar da ke nuna cewa hukuncin ta na nan daram, kuskure ne aka samu
a takardun, amma hakan bai hana jama’ar Kano nuna shakku da kuma bayyana fushin
su ta hanyar zanga-zanga ba.

 

A wani labarin na daban duk a
jihar Kano na cewa al’ummar Unguwar Kurna da Rijiyar Lemo a karamar hukumar Dala,
sun rufe hanyoyi tare da kone-konen tayoyi da kuma zanga-zanga don nuna fushin
su game da zargin wani dan sanda da harbin matashin dan wasa na kungiyar
kwallon kafa ta Kurna Samba Alhaji Salisu Rabi’u tare da karin wasu mutane
biyu.

 

Har yanzu babu wani martani game
da hakan daga jami’an tsaro, sai dai kuma rahotanni na cewa matasan sun rufe
unguwar ba shiga ba fita.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe daga ranar 18 ga Agusta a Nijeriya

Hukumar Zaɓen Nijeriya INEC ta sanar da ranar 18 ga watan Agusta, 2025 a matsayin ranar da za ta fara sabuwar rijistar katin zaɓe a...

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Mafi Shahara