DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wata kungiya ta dauki nauyin lauyoyi 300 da za su taimaka wa Matawalle a kotun koli kyauta

-

Wata kungiyar ‘yan kishin kasa (Association Of Concerned Citizens) ta yi alkawarin hada kan lauyoyi masu zaman kansu akalla 300 domin bayyana ra’ayinsu na kare dan takarar gwamna a jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Bello Mattawale, a kotun koli.
Wannan lamari dai ya biyo bayan matakin da Gwamna Dauda Lawal da jam’iyyar sa ta PDP suka dauka na zuwa kotun koli bayan umarnin kotu ya sa a sake yin zabe a kananan hukumomi uku: Maradun, Birnin-Magaji, da Bukkuyum a jihar.
Da suke jawabi a taron manema labarai a Abuja ranar Lahadi, Shugaban kungiyar Comr Ekemini Bassey, ya bayyana cewa sun dauki matakin na hada kan kwararrun lauyoyi 300 domin kare martabar dimokuradiyyar Nijeriya da kuma abin da mutane suka zaba, inda suke zargin a zaben na jihar Zamfara akwai magudin zabe da kuma masu yunkurin tsoratar da bangaren shari’a.
Kwamared Bassey, ya jaddada cewa dole ne kotun koli ta tabbatar da adalci domin kare martabarta, tare da kawo karshen girman kan wadanda suke ganin su ne ke rike da jihar Zamfara.
“Mun tattaro gungun lauyoyi da ‘yan gwagwarmaya masu fafutukar tabbatar da gaskiya da adalci, kuma zamu tsaya tsayin daka har sai kotu na mana adalci kamar yadda muka san dama kotun adalai ne, muna kuma kara jaddada hada kai da neman adalci ga Gwamna Bello Matawalle mai jiran gado a karo na biyu”. inji shi. 
Ekemini ya bukaci kotun ta koli da ta yanke hukuncin ba tare da tsoro ba domin tabbatar da adalci ga alummar jihar Zamfara akan abunda suka zaba. 
Ya kuma yi kira ga al’ummar jihar da su kwantar da hankulan jama’a, tare da nuna kwarin guiwar cewa za a yi adalci, yana mai cewa, “Bello Mattawalle zai dawo kan kujerarsa domin shine mai tausayin al’ummah, kuma wannan kungiya za ta tsaya masa tun daga farko har karshe, domin mun riga munyi bincike mun san wanene Bello Matawalle da kuma irin fadi tashin da yakeyi domin cigaban jihar zamfara ne a gabanshi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara