DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya Dakatar da Minister Jinkai, Betta Edu nan take.

-

 Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya dakatar da ministar jin ƙai, Betta Edu nan take.

Google search engine

Kakakin shugaban Najeriyar, Ajuri Ngelale ne ya sanar da matakin dakatar da ministar cikin wata sanarwa da aka fitar a yau.

Shugaba Tinubu ya ɗauki matakin ne domin ba da dama ga hukumar EFCC mai yaƙi da cin hanci da rashawa ta gudanar da bincike a kanta.

Wasu yan Najeriya sun yi ta kiraye-kiraye ga gwamnati ta dakatar da ita daga mukaminta nata domin a gudanar da cikakken bincike game da zarge-zargen da ake mata.

Ana zargin ta da bayar da umarnin tura kuɗi kimanin naira miliyan 585 zuwa wani asusun banki da babban akanta janar na ƙasa yaki amincewa da shi.

Shugaba Tinubu a sanarwar da ta fito daga fadar sa ya umurci shugaban hukumar EFCC ya gudanar da bincike sosai kan zargin da ake wa Beta Edun.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

INEC na duba buƙatun kungiyoyi 110 da ke neman rigista a matsayin jam’iyyun siyasa a Najeriya

Hukumar zabe ta kasa INEC ta bayyana cewa ta karɓi wasikun buƙatun rajistar sabbin jam’iyyu 110 daga kungiyoyi daban-daban har zuwa Litinin, 23 ga watan...

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam’iyyar na kasa

PDP ta maido wa Samuel Anyanwu mukaminsa na sakataren jam'iyyar na kasa Jam’iyyar PDP ta dawo da Samuel Anyanwu a matsayin sakataren jam’iyya na kasa bayan...

Mafi Shahara