DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan ta’adda sun kai hari sansanin sojoji a Katsina

-

‘Yan ta’adda sun kai hari a sansanin sojoji da ke kauyen Nahuta na karamar hukumar Batsari a jihar Katsina
Majiyar DCL Hausa ta ce lamarin ya faru da misalin karfe 11 na daren Lahadi wayewar Litinin, inda maharan suka shiga cikin gari suka debi dukiyoyin al’umma.
Bayanai sun ce maharan sun yi nasarar kona motocin sojojin guda biyu.
Kazalika, an ga wasu daga cikin mutanen kauyen Nahuta su na barowa a cikin motoci su na dawowa Batsari a wani abu kama da gudun hijra.
Bai dai fi kilomita 7 daga kauyen Nahuta zuwa cikin garin Batsari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kamfanin NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar man birnin Port Harcourt

Kamfanin man fetur na Nijeriya NNPCL ya musanta labarin cefanar da matatar mai ta Fatakwal ga yan kasuwa A Yayin wani taro da kamfanin ya gabatar...

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Mafi Shahara