DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda gwamnatin Kebbi ta tube rawanin Hakimai

-

 

Google search engine
Gwamnan jihar Kebbi Dr. Naisr Idris

Gwamnatin Kebbi ta sallami wasu dagatai guda uku da ke karkashin
masarautar Gwandu daga kan mukaman su, a sakamakon kama su da laifin cin amanar
gwamnati, barin guraren aikinsu ba tare da izini ba, wasa da aiki da kuma cin
hanci da karbar rashawa.

Da yake sanar da sallamar dagatan guda uku shugaban
hukumar kula da kananan hukumomi ta jihar Alhaji Masur Shehu ya ce kokar ta su
na karkashin dokokin kula da da’ar ma’aikata ta jihar.

Dagatan da aka kora sun hadar da Alhaji Lawal Yakubu,
Mai Arewan Yeldu da Malam Ahmed Sani Sarkin Gabas din Geza da kuma Alhaji Tukur
Aliyu Jagwadejin Bakuwe.

Shehu ya ce hukumar ta jima tana bibiyar ayyukan dagatan kuma ta
tattara gamsassun hujojjin da suka tabbatar da cewa kora ce kadai hukuncin su.

Ya kuma ce kafin daukar wannan mataki
sai da gwamnati ta tuntubi majalisar masu rike da sarautar gargajiya, kuma suka
bada wannan shawara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Mafi Shahara