DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Yadda wani dan sanda ya ki karbar tayin cin hancin naira miliyan 1 daga hannun mai garkuwa da mutane

-

Wani dan sanda da ke aiki karkashin rundunar yan sanda ta jihar Kaduna ya
ki karbar cin hancin Naira miliyan 1 da wani kwararren mai garkuwa da mutane ya
bashi.

Google search engine

 

Bayanai sun ce yan sanda sun yiwa dan
garkuwa da mutanen kofar rago ne a wani Otal mai suna Tafa, kuma nan take yayi wa
dan sandan tayin naira miliyan 1 cikin kudin fansar da ya karba, sai dai dan
sandan ya ki karba.

Ko da yake jawabi mai magana da yawun rundunar yan sandan jihar ASP Mansir
Hassan ya ce sun sami bayanan sirri ranar 19 ga watan da muke ciki na Agusta
cewa dan garkuwa da mutanen ya sauka a wannan Otal din nan take kuma suka aike
da jami’an su inda suka kama shi.

ASP Mansir ya ce an yi nasarar kwato sama
da naira miliyan 2 da dubu 350 a hannun mai garkuwa da mutanen da aka bayyana
sunan sa da Bello Muhammad mai shekaru 28 dan asalin jihar Zamfara.

Rahoton binciken farko-farko na yan sanda
ya nuna yadda dan bindigar ya shaida musu cewa yana cikin ‘yan ta’adda da ke
addabar yankin dajin Kagarko na jihar Kaduna.

 

 

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tattalin arzikin Najeriya zai bunkasa daga 2025 zuwa 2026 – IMF

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya sabunta hasashensa kan ci gaban tattalin arzikin Najeriya, inda ya ce zai kai kashi 3.4 cikin 100 a shekarar...

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Mafi Shahara