DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya umurci a fito da abinci domin raba wa mazauna Abuja

-

 Tinubu ya umurci a fito da abinci domin raba wa mazauna Abuja

Google search engine

 Shugaba Bola Tinubu ya umurci Ministan Babban Birnin Tarayya, Nyesom Wike, da ya gaggauta sakin hatsi da kayan abinci ga jama’ar gari, domin dakile illar tabarbarewar tattalin arziki.

 Karamar ministar babban birnin tarayya, Dakta Mariya Mahmoud, ce ta bayyana hakan a ranar Larabar da ta gabata, a wani taron gaggawa da ta yi da masu ruwa da tsaki da shugabannin kananan hukumomi shida na babban birnin tarayya Abuja.

 Ta ce umarnin ya zo ne a wata wasika daga fadar shugaban kasa, ta hannun hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa zuwa ga ministar babban birnin tarayya Abuja, yayin da ta kuma sanar da kafa kwamitin da zai aiwatar da wannan umarni cikin makonni biyu masu zuwa.

 A ranar Lahadin da ta gabata ne wasu mazauna babban birnin tarayya Abuja suka kai hari a wani dakin ajiyar kaya da ke unguwar Gwagwa-Tasha a Abuja, mallakin sakatariyar harkokin noma da raya karkara ta babban birnin tarayya Abuja, inda suka yi awon gaba da kayan abinci tare da lalata ginin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Yan kasuwar mai sun sauke farashin man fetur kasa da yadda Dagote ke sayarwa

Wasu masu shigo da man fetur daga ƙasashen waje sun fara sayar da shi a ƙasa da Naira 860 kowace lita, lamarin da ya sauka...

Saurayi ya gaggabe wa budurwarsa hakora shida a Legas

Wani saurayi a unguwar Ibadan dake Ebute Meta, jihar Legas, ya lakadawa budurwarsa Fatima, wadda ke sana’ar gyaran kai, dukan da ya janyo ta rasa...

Mafi Shahara